BloggingNews

An Dage Zuwan Buhari Kano Zuwa Wani Lokaci – Gwamnatin Kano

Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya ce sun aika wa fadar shugaban ƙasar Najeriya cewa, sun ɗage ziyarar da aka tsara Shugaba Muhammadu Buhari zai yi a Jihar domin buɗe wasu manyan ayyukan raya ƙasa.

Cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na gwamnan Abba Anwar ya fitar ranar Asabar, ya ce Ganduje ya bayyana hakan ne yayin wani taro da malamai da shugabannin siyasada sauran masu ruwa da tsaki a gidan gwamnati, ya ce an dauki matakin ne domin kaucewa faruwar abin da ba zai yi daɗi ba.

Advertisement
Advertisement

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button