News
Trending

An Sanar Da Dawowan Jirgin Kasa Daga Abuja Zuwa Kaduna

Hukumar ta dakatar da dukkan jigilar fasinjoji kan wannan hanyar ne a ranar Juma’a 27 ga watan nan na Janairu 2023 a sanadiyyar gocewan da wani jirgin kasa yayi a kusa da tashar Kubwa cikin wannan yinin.

Cikin wata sanarwa da daraktan gudanarwa na NRC Niyi Alli ya sanya wa hannu, hukumar za ta koma daukan fasinjoji daga Talata 31 ga watan Janairun 2023.

Ta kuma sanar da jadawalin jiragen da za su rika zirga-zirga kamar haka: AK1 zai tashi daga Idu da karfe 7:00 na safe KA2 zai tashi daga Rigasa da karfe 10:15 na safe AK3 zai tashi daga Idu da karfe 1:20 na rana KA4 zai tashi daga Rigasa da karfe 4:30 na yamma.

Advertisement
Advertisement

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button